Zargin badaƙala: Kotu ta hana Hadi Sirika fita ƙasar waje

A ranar Alhamis ne babbar kotun birnin tarayya Abuja ta hana tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika, diyarsa Fatimah da sirikinsa Jalal Hamma fita kasar waje.

Mai shari’a Sylvanus Orji ya yanke hukuncin cewa ba za su bar kasar nan ba har sai an kammala shari’ar da suke yi ta zambatar naira biliyan 2.7.

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, ya gurfanar da su ne a ranar Alhamis a kan tuhume-tuhume shida da ke da alaka da zamba na N2.7bn.

An gurfanar da su ne tare da Al-Buraq Investment Ltd.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta yi zargin cewa Sirika ya ci zarafin ofishinsa ta hanyar ba da kwangilar N1.3bn ga kamfanin Nigerian Air Start-up to Tianero Nigeria Limited.

More News

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...