Ƴan bindiga sun yi ta’adi a ƙauyen Zamfara

Akalla mutane uku ne aka kashe, yayin da wasu sama da 51 ciki har da wani hakimi aka yi garkuwa da su a wasu sassan jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki kauyen Bagega, wani kauye mai hakar ma’adinai a jihar, inda suka yi ta harbe-harbe a kai a kai, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutanen kauyen uku.

Rundunar ƴan sanda ba ta ce komai a kan lamarin ba saboda jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan, ASP Yazid Abubakar, bai amsa kiran da aka yi masa ba.

Sai dai Sarkin Kauyen Malam Abubakar Uba ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Reuters faruwar lamarin.

Ya ce ‘yan bindigar sun yi garkuwa da hakimin yankin kafin su ci gaba da yin garkuwa da mutane da dama a kauyen.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...