Zan bar Najeriya fiye da yadda na same ta – Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa tana da kudurin ganin ta bar mulkin kasar fiye da yadda ta karbi mulkinta.

Shugaban ya kuma bukaci ‘yan kasar da su yi wa gwamnatinsa adalci a kan irin abubuwan da ta cimma zuwa yanzu, musamman ma alkawuran da ta yi kafin zaben 2015.

Shugaban ya yi wadannan kalamai ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Jema’a, Alhaji Muhammadu Isa II, a Kafanchan, yayin da ya je jihar Kaduna ziyarar kwana biyu domin kaddamar da wasu ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]