Zan bar Najeriya fiye da yadda na same ta – Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa tana da kudurin ganin ta bar mulkin kasar fiye da yadda ta karbi mulkinta.

Shugaban ya kuma bukaci ‘yan kasar da su yi wa gwamnatinsa adalci a kan irin abubuwan da ta cimma zuwa yanzu, musamman ma alkawuran da ta yi kafin zaben 2015.

Shugaban ya yi wadannan kalamai ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Jema’a, Alhaji Muhammadu Isa II, a Kafanchan, yayin da ya je jihar Kaduna ziyarar kwana biyu domin kaddamar da wasu ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.

More News

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...