Yanzu-Yanzu: Gwamnoni sun rage yawan yan takarar APC zuwa mutum uku

Labaran da suke fitowa daga wurin taron zaben fitar da gwani na dan takarar shugaban kasa a jam’iyar APC dake gudana yanzu haka a Abuja sun bayyana cewa gwamnonin jam’iyar sun sake rage yawan yan takarar shugaban kasa a jam’iyar ya zuwa uku.

Tun da farko gwamnonin sun rage yawan yan takarar zuwa biyar kafin daga bisani su sake bada shawarar rage su zuwa uku.

Shugaban kasa Muhammad Buhari shi ne ya nemi gwamnonin da su shawo kan sauran yan takara da su hakura su janye takarar su.

Matakin na gwamnonin baya na nufin ragowar yan takarar basu da ikon shigar takara ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]