Yan Najeriya Sun Kasa Gane Ayyukan alkhairin Da Buhari Yayi Musu – Lai Mohammed – AREWA News

Alhaji Lai Mohammed ya bayyana nadamarsa guda ɗaya da yake a matsayinsa na minista.

A cewarsa, nadamar tasa bai wuce yadda wasu ƴan Najeriya ke ƙin yabawa gwamnati duk da irin namijin ƙoƙarin da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ke yi da ɗan abin da ke a hannunsa.

Lai Mohammed, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta musamman da kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Abuja.

Ya ce duk da ƙarancin kuɗaɗe, babu gwamnatin da ta taɓa kafa tarihin gwamnatin Buhari a gwamnatocin baya a Najeriya.

Musamman wajen ƙirƙiro tsare tsare da shirye-shirye da zasu kawar da talauci tsakanin mabuƙata da mata har ma da samar da ayyukan yi ga matasa.

Ministan ya ce nadamarsa ita ce wasu ƴan Najeriya sun gaza yaba ƙoƙarin da gwamnatin ke yi, amma suna murna da abubuwan da ba dai-dai ba.

Babbar nadamata a wannan gwamnatin shine ƴan Najeriya sun gaza yabawa abubuwan da gwamnati ke yi da kuɗaɗe ƙalilan.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]