Kotu ta bayar da  umarnin kama Mamman tsohon ministan wutar lantarki a gwamnatin Buhari

Babbar kotun birnin tarayya Abuja ta bayar da sammacin kama Saleh Mamman tsohon ministan wutar lantarki bayan da ya gaza bayyana kansa a gaban kotun.

A zaman kotun na ranar Litinin, Maryam Anineh alkaliyar kotun  ta soke belin da  tun da farko aka bawa Mamman.

Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati na tuhumar tsohon ministan tare da wasu mutane bakwai kan zargin su da haɗa biki da yin almundahanar kuɗaɗe da yawansu ya kai naira biliyan 31.

Har ila yau Mamman na fuskantar wasu tuhume-tuhumen a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja.

Ya rike mukamin wutar lantarki a gwamnatin marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammad Buhari daga shekarar 2019 ya zuwa 2021.

More from this stream

Recomended