’Yan Najeriya Sun Amince Gwamnatin APC Ta Gaza – ADC

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ce ’yan Najeriya sun cimma matsaya cewa gwamnatin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta gaza wajen tafiyar da mulkin ƙasar.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi, ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na tashar Channels Television.

A cewarsa, ya rataya a wuyan jam’iyyun adawa su tabbatar wa ’yan Najeriya cewa suna da ingantattun hanyoyi da dabaru da za su fi na gwamnatin da ke kan mulki.

ADC ta ce irin waɗannan matsaloli na nuna gazawar shugabanci, tare da jaddada buƙatar sauyi a tafiyar da harkokin ƙasar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]