‘Yan majalisar dattawa sun nemi sojoji su datse hanyoyin da barayin daji suke tserewa

‘Yan majalisar dattawan Najeriya sun umarci sojoji da sauran jami’an tsaron kasar da su sanya ido sosai tare da datse hanyoyin da ‘yan ta’adda da barayin daji ke bi suna tserewa domin hana su komawa wasu sassan kasar.

Majalisar ta bayar da umarnin ne bayan gabatar da kuduri da mataimakin Gagarabadau, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, na jihar Neja ya yi sakamakon sabbin hare-hare da satar mutane da ake yi a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu na jihar Naija.

Sanatan ya ce sakamakon muggan hare-haren da sojoji da sauran jami’an tsaro ke kai wa ‘yan ta’adda da barayin daji da suka addabi yankunan gabashin jihar Sokoto da Zamfara, ‘yan ta’adda na ta tserewa suna shiga jihar Naija.

A don haka ya ce ya kamata a tsara hare-haren da ake kai wa ‘yan ta’addar da kyau yadda ya kamata ta yadda za a datse duk wata hanya da suke bi suna guduwa suna shiga sassan jihar Naija.

Majalisar kamar yadda jaridar DailyTrust ta ruwaito ta kuma umarci hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya da ta samar da kayan abinci da sauran muhimman abubuwa na jin dadi ga mutanen kauyukan da hare-haren ‘yan ta’addar ke shafa da kuma ‘yan gudun hijira a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu.

More News

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Majalisar dokokin Zamfara ta tsige kakakinta saboda tsanantar rashin tsaro a jihar

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige kakakinta, Bilyaminu Moriki, tare da nada Bashar Gummi, a matsayin kakakin majalisar. Hakan ya biyo bayan kudirin da dan...

Ƴan bindiga sun kashe mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da kisan mutane shida da wasu ‘yan bindiga suka yi a karamar hukumar Faskari a jihar. Jami’in hulda...

Sace-sacen motoci ya yawaita a Adamawa—Ƴan sanda

Ana ci gaba da samun karuwar sace-sacen motoci a jihar Adamawa, kamar yadda rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar. Rundunar ‘yan sandan ta bayyana haka...