Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe wasu ‘yan uwa guda biyu a garin Gajere da ke karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.
Wadanda lamarin ya rutsa da su lokacin da suke aiki a gonakinsu, inda rahotanni suka ce lamarin ya faru ne da safiyar Juma’a.
Ku tuna cewa akalla mutanen kauyen 10 ne ‘yan bindigar suka yi garkuwa da su a cikin makonni biyun da suka gabata.
Wata majiya ta bayyana cewa ‘yan bindigar da ke zagayawa sun yi ta addabar yankin inda suka yi garkuwa da mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, tare da kwashe shanunsu.
Shi ma dan majalisar jiha mai wakiltar mazabar Kakangi Yahaya Musa ya tabbatar da kisan na baya bayan nan.
Dan majalisar ya bayyana alhininsa da faruwar lamarin yayin da yake jajantawa wadanda abin ya shafa da kuma iyalansu.