‘Yan bindiga sun kashe kwamishina a Katsina da masallata 16 a Neja

Labari da dumi-dumi

Rahotanni daga jihar Katsina a arewacin Najeriya na cewa ƴan bindiga sun kashe wani kwamshina a jihar Katsina a arewacin Najeriya.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar ya tabbatar da lamarin a wani taron manema labarai a ranar Alhamis cewa lamarin ya faru ne a ranar Laraba da daddare.

Sannan wasu rahotannin daga jihar Neja a arewa ta tsakiyar ƙasar kuma ƴan bindigar sun kashe mutum 16 a masallaci wasu goammai kuma sun jikkata a wani hari da ‘aka kai ƙauyen Ba’are a karamar hukumar Mashegu da ke jihar Nejan.

Ahmed Ibrahim Matane shi ne sakataren gwamnatin jihar ta Neja, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:30 na safiyar ranar Laraba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]