‘Yan bindiga sun kashe kwamishina a Katsina da masallata 16 a Neja

Labari da dumi-dumi

Rahotanni daga jihar Katsina a arewacin Najeriya na cewa ƴan bindiga sun kashe wani kwamshina a jihar Katsina a arewacin Najeriya.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar ya tabbatar da lamarin a wani taron manema labarai a ranar Alhamis cewa lamarin ya faru ne a ranar Laraba da daddare.

Sannan wasu rahotannin daga jihar Neja a arewa ta tsakiyar ƙasar kuma ƴan bindigar sun kashe mutum 16 a masallaci wasu goammai kuma sun jikkata a wani hari da ‘aka kai ƙauyen Ba’are a karamar hukumar Mashegu da ke jihar Nejan.

Ahmed Ibrahim Matane shi ne sakataren gwamnatin jihar ta Neja, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:30 na safiyar ranar Laraba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]