Yadda aka yanke wa masu satar mutane hukuncin É—aurin rai da rai a Sokoto

Police

Asalin hoton, Getty Images

Ƴan uwa da masu rajin kare haƙƙin É—an adam sun bayyana ra’ayoyinsu kan hukuncin É—aurin rai-da-rai da Babbar Kotun Tarayya ta yanke wa wasu masu garkuwa da mutane huÉ—u a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Kotun dai ta yanke musu wannan hukunci ne bayan ta same su da laifin garkuwa da wani fitaccen É—an kasuwa a shekarar 2013, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa saboda jigata da É—imautar da ya yi.

Ba kasafai ake jin kotuna na yanke wa masu satar mutane hukunci irin wannan hukunci ba, musamman a yankin arewacin Æ™asar, inda hare-haren Æ´an fashin ke Æ™ara ta’azzara.

Duk da tsawon shekarun da aka kwashe bayan sacewa tare da yin garkuwa da marigayi Alhaji Abubakar Dankure, makusantan É—an kasuwar sun ce É—aurin rai-da-rai da kotu ta yanke wa masu garkuwar ya rage musu zafi da raÉ—aÉ—in aika-aikar da aka tafka musu.

Ɗaya daga cikin ƴaƴan marigayin Alhaji Aminu Abubakar Dankure ya ce, ko da yake hukuncin ba zai iya cike giɓin da mutuwar mahaifinsu ta bari ba, amma dai sun samu ƙwarin gwiwar cewa an kamanta adalci.

“Hukunci dai kamar yadda aka yi shi, mun gode Allah. Kuma babu wani abu da bai yi mana daidai ba cikin hukuncin.”

Sai dai ya ce duk da cewa sun ji daÉ—in hukuncin hakan ba zai goge tabon rashin uba da suka yi ba, “sai da i hakan ya fi da a ce haka aka Æ™yale su.”

Masu garkuwa sun sace mahaifinsu Alhaji Abubakar Dankure inda ya shafe kwana shida a hannunsu.

Daga bisani bayan biyan kudin fansa ne suka sake shi, sai dai kuma sakamakon jigata da ya yi sai Allah ya yi masa rasuwa bayan ‘yan kwanaki.

Jami’an tsaro sun yi nasarar kama masu laifin su shida, ko da yake biyu sun rasu, inda aka gurfanar da su a gaban Kotun Tarayya a 2013.

Bayan saÉ“ata-juyata irin-na shari’a kusan tsawon shekara takwas a makon jiya, Mai Sharia Lurwanu Aikawa na Babbar Kotun Tarayya da ke Sokoto ya yanke musu hukuncin daurin rai-da-rai.

Barista Labaran Sha’aibu Magaji lauyan masu Æ™ara, ya ce: “Ya kamata a sanar da masu sauraro cewa akwai mutum biyu daga cikinsu da suka mutu yayin da ake tsare da su saboda dalili na rashin lafiya.

“Yanzu saura su hudu kenan da aka yanke wa hukuncin É—aurin rai da rai.

Bayan hukuncin ɗaurin, kotu kuma ta bayar da umarni su mayar da kuɗaɗen da suka karɓa na fansa har dala dubu 300.

“Na biyu kotu ta yanke hukuncin cewa su bai wa iyalan marigayin kuÉ—i naira miliyan 50 don rage musu damuwa na halin da suka fuskanta yayin da aka sace mahaifin nasu.

“Kana an sake umartarsu da ba da naira dubu É—ari-É—ari ga Alhaji Aminu Dankure da Nasiru, da zai zamanto a madadin kudin jirgi da suka biya na zuwa Abuja don biyan kuÉ—in fansar baban nasu a Kwali,” a cewar lauyan.

Masu rajin kare hakkin dan adam ma, sun tofa albarkacin su game da wannan hukunci. Barista Muhammad Mansur Aliyu na daga cikinsu, kuma ya ce hukuncin abu ne mai daÉ—i.

“Hukuncin ya yi wa al’umma da kuma mu kanmu lauyoyi daÉ—i saboda ya tura saÆ™o na musamman ga dukkan wanda yake wannan aiki na satar al’umma.

“Saboda an yanke musu hukuncin cewa lallai za su zauna gidan yari har Æ™arshen rayuwarsu. Ka ga kuwa ai lallai kowa zai ji daÉ—in haka.”

Mutum hudun da aka yanke wa hukuncin dai, suna da damar daukaka kara nan da kwana 90.

Lamarin masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa na ci gaba da ta’azzara a Najeriya.

Hakan ce ta a watan Yulin bara Majalisar Dattawan kasar ta amince da hukuncin daurin rai-da-rai ga duk wanda aka kama da laifin garkuwa da mutane a kasar.

A baya dai ana yanke hukuncin daurin shekara 10 ne ga mutanen da aka kama da laifin.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...