Wike: Tinubu Na Yin Barci Cikin Kwanciyar Hankali Saboda Ayyukan Da Gwamnatinsa Ke Yi



Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na yin barci cikin kwanciyar hankali saboda irin ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa a Abuja da sauran sassan Najeriya.

Wike ya yi wannan furuci ne a ranar Laraba yayin ƙaddamar da titin Arterial Road N5 da ke Abuja.

A cewarsa, idan kyakkyawan shugabanci da sauye-sauyen da gwamnati ke kawowa su ne ma’aunin samun goyon bayan jama’a, to gwamnatin Tinubu ta riga ta nuna tasirinta a Babban Birnin Tarayya.

Ministan ya ƙalubalanci duk wani mazaunin FCT da ya fito ya ce bai ga ayyukan gwamnati ko amfaninsu ba.

Wike ya kuma tuna cewa aikin titin ya fuskanci ƙalubale a baya saboda rikicin diyya ga waɗanda rushewar gine-gine ta shafa, amma daga bisani an warware matsalar, lamarin da ya ba da damar ci gaba da aikin.

More from this stream

Recomended