Wata ta maka mahaifinta a kotu saboda zai mata auren dole

Wata matashiya ƴar shekara 20 mai suna Fatima Aliyu ta kai mahaifinta kotu kan kokarin yi mata auren dole.

Fatima daga garin Kaduna ta shaida wa kotun shari’ar Musulunci cewa tana da wanda take so, amma mahaifinta ke kokarin yi mata auren da ba ta so.

A cewar mahaifin, kakanninta ne suka zaɓa wa diyar tasa mijin aure kafin rasuwarsu, shi ya sa yake kokarin cika alkawari.

Alkali Malam Aiyeku Abdulrahman, ya ce duk da yake mahaifi na da damar zaɓawa ‘yarsa mijin aure, a wannan gabar kokarin tilasta mata bai dace ba.

Alkalin ya bukaci mahaifin ya bai wa ‘yarsa damar gabatar da mutumin da take so, sannan a yi bincike, idan babu wani laifi to a bar su su yi aurensu.

More from this stream

Recomended