Wata ƙungiya ta ba wa Atiku shawarar kar ya fito takara a 2027

Wata kungiya a cikin jam’iyyar PDP, CPDPL, mai suna Concerned PDP League, ta yi kira ga Alhaji Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023 da kada ya sake tsayawa takara a 2027.

Shawarar kungiyar na kunshe ne a cikin wata sanarwa.

Sakatariyar kungiyar ta kasa, Alhaji Tasiu Muhammed da kuma mukaddashin daraktan yada labarai da sadarwa na kasa, Gbenga Adedamola, ne suka sanya wa hannu a ranar Lahad.a Abuja.

CPDPL ta kuma bukaci shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, da kada ya sanya wani buri na neman kujerar shugaban kasa har sai 2031, don kauce wa sake faruwar abin da ya faru da jam’iyyar a 2015 da 2023.

A cewar kungiyar, shawararta ta kasance wani abin tuni ne ga masu sha’awar yin mulki daga Arewa su fahimci cewa Kudu tana da shekaru takwas kafin mulki ya dawo Arewa a 2031.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...