Wasu sanatocin APC sun goyi bayan tsige Buhari

Adamu Bulkachuwa,sanata mai wakiltar mazabar Bauchi ta arewa a majalisar dattawa ya ce da yawa daga cikin abokan aikinsa na jam’iyyar su ta APC sun goyi bayan yunkurin tsige shugaban kasa, Muhammad Buhari.

A makon da ya wuce ne sanatocin da suka fito daga jam’iyyar PDP da wasu jam’iyun adawa suka bawa shugaban kasar wa’adin mako 6 kan ya shawo matsalar tsaro ko kuma su tsige shi.

Da yake magana a gidan talabijin na Channel a ranar Litinin, Bulkachuwa ya ce barazanar tsigewar ita ce mataki na karshe da ya zama dole yan majalisar su dauka.

Ya ce shi da abokan aikinsa sun gwada taimakawa bangaren zartarwa dama shi kansa shugaban kasa ta hanyoyi da dama domin magance matsalar tsaro a kasarnan amma abin ya ci tura.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...