Wani Likitan Hakori A Italiya Ya Yi Yunkurin Bada Hannun Roba Don Karban Allurar Rigakafin Covid

Wata ma’aikaciyar jinya a birnin Biella da ke arewacin kasar, Filippa Bua, ta ce nan da nan ta gano saboda jikinta bai bata ba yayin da wannan mutum ya mika hannunsa don karbar allurar a ranar Alhamis.

“Lokacin da na gano hannun, na ji fatar da sanyi da kuma gumi, kuma launin fatar ya yi haske sosai,” Bua ta shaida wa jaridar Italiya Corriere della Sera.

Ta ce da farko ta yi tunanin mutumin mai shekaru 57 yana da irin hannun roban ga ake sa wa wandanda aka yanke masu hannu ne kuma ya yi kuskuren bayar da hannun da bai dace ba. Tuni ta daga rigarsa ta gano hannun silicone roba.

“Nan da nan na fahimci cewa mutumin yana kokarin gujewa allurar ne ta hanyar amfani da hannun roba ta silicone, inda yake fatan zan yi masa allurar, ba tare da sani na ba,” in ji Bua.

Ma’aikacin jinyar ta ce mutumin ya yarda cewa ba ya son allurar rigakafin amma kuma yana nema samun takardar izinin tafiya wurare daban-daban”, wanda daga ranar Litinin za a bukaci amfani da takardar shiga gidajen cin abinci, sinima, da dai sauran wuraren shakatawa a Italiya.

Tuni dai aka dakatar da shi daga aiki saboda kin yin allurar da Italiya ke bukata ga duk ma’aikatan lafiya.

Ma’aikaciyar jinyar ta ce mutumin ya kasance mai ladabi kuma ya bar cibiyar allurar bayan yunkurin da ya kasa yi.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...