UAE ta kawo ƙarshen dokar hana ƴan Najeriya biza bayan Tinubu ya kai ziyara Abu Dhabi

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi nasarar kulla wata yarjejeniya mai cike da tarihi tsakanin Najeriya da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), wanda ya kawo karshen dokar hana bizar da ta yi wa ƴan Najeriya.

An samu nasarar ne a ziyarar da shugaba Tinubu ya kai Abu Dhabi, bayan halartar taron kasashen G-20 da ya gudana a kasar Indiya.

Muhimmin abin ya faru ne lokacin da Ambasada Designate, Amb Salem Saeed Al-Shamsi, ya gabatar da wasiƙarsa ga shugaba Tinubu a Aso Rock, Nijeriya.

Shugaban kasar bai bata lokaci ba wajen jagorantar warware takaddamar diflomasiyya da ta dade tana wanzuwa.

Mai magana da yawun shugaban kasar, Cif Ajuri Ngelale, ya bayyana cikakken bayanin yarjejeniyar a cikin wata sanarwa a ranar Litinin, yana mai bayyana ganawar da mahukuntan UAE a matsayin mai matukar fa’ida.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...