Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa kasarsa za ta dauki mataki bayan da ya zargi Iran da harbo wani jirgin yakin Apache na Amurka a mashigar Hormuz.
Trump ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Truth Social a ranar Talata. Ya ce jami’an sojin Amurka sun sanar da shi cewa lamarin ya faru ne cikin dare yayin da jirgin ke sintiri a yankin.
A cewarsa, matukan jirgin biyu sun tsira kuma ba su samu wani rauni ba.
Trump ya ce harin da ake zargin an kai wa jirgin ba zai wuce ba tare da martani daga Amurka ba.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin na iya kara dagula dangantaka tsakanin Amurka da Iran, musamman a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan tsaro a mashigar Hormuz, wadda ke daga cikin muhimman hanyoyin jigilar man fetur a duniya.
Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin sojin Amurka da na Iran ba su fitar da karin bayani kan lamarin ba.
Trump Ya Yi Barazanar Martani Bayan An Zargi Iran Da Harbo Jirgin Yakin Amurka

