Tinubu zai kashe biliyoyin kuɗaɗe wajen tafiye-tafiye kasashen waje a 2026

Gwamnatin tarayya ware biliyan ₦6.14 a matsayin kuɗaɗen tafiye-tafiye zuwa kasashen waje  da shugaban ƙasa,Bola Ahmad Tinubu zai yi a shekarar 2016.

Bayanin haka na kunshe ne cikin kunshin kasafin kudin shekarar 2026.

Har ila yau kunshin kasafin kudin ya nuna cewa an ware naira miliyan ₦873.88 a matsayin kudin da za a kashe a tafiye-tafiyen da shugaban kasar zai yi a Najeriya a cikin shekarar ta 2026 hakan yasa jumullar kudin tafiye-tafiyen a cikin gida da kuma ƙasashen ketare ya kama biliyan ₦7.01.

Shima ofishin mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima an ware masa naira biliyan 1.73 a matsayin kuɗaɗen zai kashe wajen tafiye-tafiyen cikin gida da kasashen waje.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]