Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin sa ta aiwatar cikin shekaru 3 sun fara samar da ci gaba mai ɗorewa ga tattalin arzikin Najeriya.
Tinubu ya bayyana hakan ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar Deloitte Africa ƙarƙashin jagorancin Babbar Daraktar kamfanin, Ruwayda Redfearn.
Shugaban ya ce duk da cewa sauye-sauyen sun zo da ƙalubale, sun taimaka wajen ƙarfafa tushen tattalin arzikin ƙasar da kuma bunƙasa tsarin kuɗaɗe da haraji.
A nata ɓangaren, Redfearn ta tabbatar wa gwamnatin tarayya cewa kamfanin Deloitte Africa a shirye yake ya ci gaba da tallafa wa ajandar gyaran tattalin arzikin Najeriya, yayin da Babban Daraktan Deloitte West Africa, Yomi Olugbenro, ya ce kamfanin zai yi amfani da ƙwarewar da ya samu a ƙasashe daban-daban domin tallafa wa ci gaban tattalin arzikin ƙasar.
Tinubu Ya Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Fara Haifar Da Ci Gaba

