Tinubu Ya Tafi Ziyarar Aiki Ƙasashen Turai

Zaɓaɓɓen shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bar Najeriya a ranar Laraba ya zuwa ƙasashen turai inda zai fara ziyarar aiki ta wasu yan kwanaki.

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sahannun Tunde Rahman jami’in dake magana da yawun ofishin zaɓaɓɓen shugaban ƙasar ya ce Tinubu zai amfani da ziyarar wajen tsara manufofi da kuma tsare-tsaren da gwamnatinsa za ta zo da su.

Har ila yau zai yi amfani da ziyarar wajen jawo hankalin masu zuba jari a Najeriya.

Wannan ne dai karo na biyu da Tinubu yake kai ziyara ƙasashen Turai tun bayan da aka bayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen shugaban kasar Najeriya.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...