Tinubu ya rantsar da sabbin ministoci biyu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya rantsar da Bernard Doro da Kingsley Udeh a matsayin ministoci a majalisar zartarwa ta tarayya a yayin wani gajeren biki da aka yi a fadar Ado Rock.

Bikin ya gudana ne jim kadan kafin zaman  majalisar zartarwa ta tarayya da shugaban kasa Tinubu ya jagoranta a ranar Alhamis.

Doro wanda ya fito daga jihar Filato ya maye gurbin, Nentawe Yilwatda ministan ma’aikatar jin kai da yaki da talauci wanda ya yi murabus domin zama shugaban jam’iyar APC, a cikin watan Oktoba ne majalisar dattawa ta tantance tare da amincewa da Doro a matsayin minista.

Udeh ya maye gurbin, Uche  Nnaji a matsayin ministan kimiya da fasaha wanda ya yi murabus sakamakon zargin takardun karatu na jabu.

A ranar Alhamis ne majalisar dattawa ta tantance Udeh tare da tabbatar da shi a matsayin minista bayan wata yar gajeriyar tantancewa.

Kafin ya zama minista Udeh ya rike muÆ™amin kwamishinan shari’a na jihar Enugu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]