Tinubu ya gana da Tony Blair

Zaɓaɓɓen shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da tsohon Firaministan Birtaniya, Tony Blair a Abuja.

Blair shi ne shugaban cibiyar Tony Blair Institute For Good Governance

A cikin wani sako da ya wallafa Tinubu ya ce ganawar ta su ta mayar da hankali kan yadda Najeriya za ta cigaba da amfana daga ayyukan cibiyar dake fafutukar samar da gwamnati ta gari.

A yayin ganawar Tinubu na tare da mataimakinsa, Kashim Shettima da kuma kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]