Zaɓaɓɓen shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da tsohon Firaministan Birtaniya, Tony Blair a Abuja.
Blair shi ne shugaban cibiyar Tony Blair Institute For Good Governance
A cikin wani sako da ya wallafa Tinubu ya ce ganawar ta su ta mayar da hankali kan yadda Najeriya za ta cigaba da amfana daga ayyukan cibiyar dake fafutukar samar da gwamnati ta gari.
A yayin ganawar Tinubu na tare da mataimakinsa, Kashim Shettima da kuma kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila.