Tambuwal ya yi ganawar gaggawa da alummar garuruwan da aka samu bullar yan bindiga

A wani mataki ndake zama riga-kafi kan matasalar yan bindiga dake neman addabar wasu sassan jihar Sokoto gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal ya yi wata ganawa da mutanen Sabon Garin Liman dake karamar hukumar Wurno.

Ganawar da gwamnan ya yi da su na zuwa ne bayan da aka samu rahoton bullar yan bindiga a yankin.

Tambuwal ya isa garin da tawagar jami’an tsaro da suka hada sojoji, yan sanda da sauran jami’an hukumomin tsaro.

A yayin ziyarar gwamnan ya gargadi yan bindigar da kuma masu basu bayanai da su yi nesa da jihar ko kuma su fuskanci hukunci mai tsauri idan suka shiga hannu.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...