Takaddama Ta Kaure Tsakanin Amaechi Da Atiku A ADC



Takaddama ta ɓarke a cikin jam’iyyar ADC tsakanin tsohon gwamnan jihar Rivers, Rotimi Amaechi, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.

Amaechi ya bayyana cewa Atiku ba mutum ne da zai iya lashe zaɓen shugaban ƙasa ba, yana mai nuna cewa ya sha kaye a zaɓukan da ya tsaya a baya. Ya ce jam’iyyar ta fi buƙatar ɗan takarar da jama’a za su iya zaɓa.

Sai dai ɓangaren Atiku sun mayar da martani da cewa kalaman Amaechi alamar tsoro ne, domin sun yi imanin Atiku ya fi samun karɓuwa a wajen ‘yan Najeriya.

Atiku Abubakar dai ya taba yin takarar shugaban ƙasa sau huɗu a baya, kuma idan ya tsaya takara a 2027, zai zama karo na biyar kenan.

More from this stream

Recomended