Lamarin wanda ya auku a unguwar Tudun Wada dake garin Mararrabar Abuja da Nasarawa, babu tunanin aure a zuciyar yarinyar mai suna Fiddausi, inda shigar ta gida kawai sai aka ce mata ta shirya za a daura aurenta, ba tare da ta taba yin soyayya da wanda za ta aura ba.
Abinda ya faru shine, wanda ta aura ya shirya auren wata ne, inda a ranar jajiberin auren, wato jiya Juma’a, sai auren ya fasu bisa wasu dalilai, wanda hakan ya sa daya daga cikin abokan angon ya ba shi kanwarsa, wanda kuma aka daura auren ba tare da an daga ba.
An daura aure ne a yau Asabar.
Tabbas kowace mace ce ba a wannan lokaci za ta amince a yi mata irin wannan aure ba tare da wanda suka saba ba. Kuma wani abin burgewa shine amaryar ta saki jikinta an gudanar da shagulgulan biki cikin farin ciki da annushuwa ba tare da sabawa umarnin iyayenta ba.
Sannan kuma duk wani buri da take da shi game da ranar aurenta, ta ajiye shi a gefe duk don ta yi biyayya ga iyayenta.