Ta dawo daga aike aka ce da ita za a daura aurenta gobe, ta amince ba tare da saba wa umarnin iyayenta ba – AREWA News

Lamarin wanda ya auku a unguwar Tudun Wada dake garin Mararrabar Abuja da Nasarawa, babu tunanin aure a zuciyar yarinyar mai suna Fiddausi, inda shigar ta gida kawai sai aka ce mata ta shirya za a daura aurenta, ba tare da ta taba yin soyayya da wanda za ta aura ba.

Abinda ya faru shine, wanda ta aura ya shirya auren wata ne, inda a ranar jajiberin auren, wato jiya Juma’a, sai auren ya fasu bisa wasu dalilai, wanda hakan ya sa daya daga cikin abokan angon ya ba shi kanwarsa, wanda kuma aka daura auren ba tare da an daga ba.

An daura aure ne a yau Asabar.

Tabbas kowace mace ce ba a wannan lokaci za ta amince a yi mata irin wannan aure ba tare da wanda suka saba ba. Kuma wani abin burgewa shine amaryar ta saki jikinta an gudanar da shagulgulan biki cikin farin ciki da annushuwa ba tare da sabawa umarnin iyayenta ba.

Sannan kuma duk wani buri da take da shi game da ranar aurenta, ta ajiye shi a gefe duk don ta yi biyayya ga iyayenta.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...