Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu mayaƙan Boko Haram biyar a wani farmaki da suka kai maboyarsu dake jihar Borno.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro kan yankin tafkin Chadi ya ce dakarun rundunar Operation Haɗin Kai sun kashe mayaƙan ne a farmakin da suka kai a dajin Sambisa.

Bayanai da ya wallafa ya ce sojojin da haɗin gwiwa dakarun soja na musamman sun kai farmakin ne a ranar Asabar a maɓoyar ƴan ta’addar dake ƙaramar hukumar Bama.

A cewar Makama majiyar jami’an sojan sirri ta bayyana cewa wasu daga cikin ƴan ta’addar sun tsere a yayin da aka kashe biyar daga cikinsu.

An samu nasarar kwato bindigogi uku ƙirar gida, bam guda biyu na bindigar  RPG, harsashi 23, gidan zuba harsashi 1 da kuma magunguna na daga cikin abin da aka samu a tare da ƴan ta’addar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]