Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu mayaƙan Boko Haram biyar a wani farmaki da suka kai maboyarsu dake jihar Borno.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro kan yankin tafkin Chadi ya ce dakarun rundunar Operation Haɗin Kai sun kashe mayaƙan ne a farmakin da suka kai a dajin Sambisa.

Bayanai da ya wallafa ya ce sojojin da haɗin gwiwa dakarun soja na musamman sun kai farmakin ne a ranar Asabar a maɓoyar ƴan ta’addar dake ƙaramar hukumar Bama.

A cewar Makama majiyar jami’an sojan sirri ta bayyana cewa wasu daga cikin ƴan ta’addar sun tsere a yayin da aka kashe biyar daga cikinsu.

An samu nasarar kwato bindigogi uku ƙirar gida, bam guda biyu na bindigar  RPG, harsashi 23, gidan zuba harsashi 1 da kuma magunguna na daga cikin abin da aka samu a tare da ƴan ta’addar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]