Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga Biyu Tare Da Ceto Mutane 20 Da Aka Yi Garkuwa Dasu A Jihar Zamfara

Dakarun Rundunar Sojan Najeriya sun kashe ƴan fashin daji biyu ciki har da wani gawurtaccen ɗan bindiga a jihar Zamfara.

A wata sanarwa ranar Talata, Yahaya Ibrahim jami’in yaɗa labarai na rundunar Operation Hadarin Daji ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a wani farmaki da aka kai maɓoyarsu dake kananan hukumomin Zurmi da Birnin Magaji a jihar Zamfara.

Ibrahim ya ce sojojin sun ceto mutane 20 da aka yi garkuwa da su da suka haɗa da mata da kuma ƙananan yara.

Ya ce sojojin sun samu nasarar lalata maɓoyar yan ta’addar da kuma maɓoyar wani fitaccen ɗan bindiga da ake kira Sule.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...