Sojoji Sun Kama Mayaƙan Boko Haram Biyu

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai dake yaki da yan ta’adda a yankin arewa maso gabas sun samu nasarar kama wasu mayakan Boko Haram biyu.

Mayakan na Boko Haram sun fada hannun jami’an tsaron ne biyo bayan musayar wutar da aka gwabza tsakanin dakarun sojan da yan ta’addar a wajen kauyen Tumballa dake dake kusa da karamar hukumar Damboa ta jihar Borno.

A wani labarin kuma wasu mayakan na Boko Haram biyu sun mutu bayan da nakiyar da suke shirin danawa a hanyar da sojoji suke sintiri ta tashi da su a ranar Lahadi 31 ga watan Disamba.

Bam din da suke ɗanawa ya tashi da su tare da yi musu gunduwa-gunduwa a kauyen Genderi dake kan iyakar Kamaru a yankin tafkin Chadi.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...