Shugaba Buhari zai halarci taron cigaban Afrika da za a yi a kasar Japan

Shugaban kasa Muhammad Buhari zai tashi daga filin jirgin saman Abuja ranar Lahadi ya zuwa kasar Japan domin halartar taron kasa da kasa kan cigaban Afrika karo na bakwai da akaiwa lakabi da TICAD7.

Taron zai gudane ne a birnin Yokohoma daga ranar 28 ya zuwa 30 ga watan Agusta.

A wata sanarwa ranar Juma’a mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ya ce wannan ne karo na biyu da Buhari zai halarci taron bayan da ya halarci TICAD6 da aka yi a Nairobi babban birnin kasar Kenya cikin watan Agustan shekarar 2016.

Adesina ya ce firaministan kasar, Shinzo Abe shine zai bude taron.

A yayin ziyarar shugaban kasa zai samu rakiyar wasu gwamnoni da suka hada da Babagana Umara Zulum na jihar Borno,Babajide Sanwo-Olu na jihar Lagos,da kuma Abdulrahman Abdulrazak na jihar Kwara.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...