Rashin Tsaftataccen Makamashi Na Kashe Mutane Dubu Ɗari A Najeriya Duk Shekara — Tony Attah



Shugaban kamfanin Renaissance Africa Energy Company, Tony Attah, ya ce kusan mutane dubu ɗari ne ke mutuwa a Najeriya duk shekara sakamakon rashin samun tsaftataccen makamashi.

Attah ya bayyana haka ne a yayin taron Africa CEO Forum da aka gudanar a Kigali na ƙasar Rwanda. Ya ce matsalar ta shafi nahiyar Afirka baki ɗaya, inda fiye da mutane dubu ɗari huɗu ke mutuwa saboda rashin samun makamashi mai tsafta.

Ya bayyana cewa mata da yara da ke amfani da gurɓataccen mai wajen girki suna cikin waɗanda matsalar ta fi shafa.

A cewarsa, Afirka na da dimbin albarkatun iskar gas da za su iya taimakawa wajen samar da lantarki da inganta rayuwar al’umma, amma har yanzu ba a yi amfani da su yadda ya kamata ba.

Tony Attah ya kuma yi kira ga ƙasashen Afirka su fara zuba jari a albarkatun da suke da su maimakon dogaro da tallafin kuɗaɗe daga ƙasashen waje.

Ya ƙara da cewa ƙarancin lantarki na ci gaba da kawo cikas ga ci gaban tattalin arziƙin Najeriya, inda ya ce samar da wutar lantarki bai kai bukatar mutane sama da miliyan ɗari biyu da ke ƙasar ba.

More from this stream

Recomended