Rundunar ‘Yan Sandan jihar Yobe ta kama wani da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi bayan ta kai samame wata ma’ajiyar ƙwayoyi a ƙauyen Danchuwa da ke ƙaramar hukumar Potiskum.
A yayin samamen, jami’an sun ƙwato kwali 8 na miyagun ƙwayoyi iri daban-daban, buhuna 1 da rabi na allunan Tramadol da Exzol, tare da kuɗi har ₦835,500 da ake zargin kuɗaɗen safarar ƙwayoyin ne.
Rundunar ta ce wasu da ake zargin abokan wanda aka kama ne sun yi yunƙurin hana kama shi, amma jami’an sun fatattake su, duk da cewa wasu ‘yan sanda sun samu ƙananan raunuka.
A wani samame na daban, ‘yan sanda sun kama Saidu Mohammed mai shekaru 40, wanda ake zargi da jagorantar gungun masu garkuwa da mutane da fashi da makami. Rahotanni sun ce yana gudanar da ayyukansa a jihohin Bauchi, Yobe da Gombe.
Rundunar ta bayyana cewa bincike na ci gaba domin cafke sauran waɗanda ake zargi da hannu a waɗannan laifuka.
‘Yan Sandan Yobe Sun Kai Samame Ma’ajiyar Miyagun Ƙwayoyi, Sun Kama Waɗanda Ake Zargi

