Dakarun Operation Hadin Kai sun dakile wani hari da mayaƙan ƙungiyar ISWAP suka kai kan sansanin soji da ke Logomani a ƙaramar hukumar Ngala ta jihar Borno.
Rahotanni sun ce an kashe mayaƙa da dama a yayin artabun, sai dai soja 1 ya rasa ransa, yayin da wasu motocin yaƙi da kayan aiki suka lalace.
Haka kuma, dakarun sun kuɓutar da mutum 2 da aka sace a ƙaramar hukumar Askira-Uba, inda suka kuma ƙwato kuɗi da kayan da ake zargin ana amfani da su wajen tallafa wa ayyukan ta’addanci.
A wani samame na daban, mayaƙan ISWAP 6 tare da iyalansu sun miƙa wuya ga dakarun soji a yankin Gwoza.
A jihar Zamfara kuma, jami’an tsaro sun ceto wani ma’aikacin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da aka sace, tare da ƙwato shanu masu yawa da ‘yan bindiga suka sace.
Rundunar sojin ta ce waɗannan hare-hare da samame na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na rusa cibiyoyin ‘yan ta’adda da dawo da zaman lafiya a Arewa maso Gabas da sauran yankunan da matsalar tsaro ta shafa.
Dakaru Sun Dakile Harin ISWAP Kan Sansanin Soji A Borno

