SERAP Ta Shigar Da Buhari, Lai Mohammed Kara A Kotu – AREWA News

VoA Hausa

Kungiyar SERAP mai gwagwarmayar yaki da cin hanci da rashawa da tabbatar da adalci a Najeriya, ta shigar da hukumomin kasar kara a gaban wata babbar kotun Abuja.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na Facebook, SERAP ta ce ta nemi kotun da “ta dakatar da gwamnatin Najeriya da Ministan yada labarai Mr. Lai Mohammed daga umarnin da suka bayar wanda ya sabawa doka, inda suka ba kafafen talabjin da na rediyo umarnin su goge shafinsu na Twitter.”

Kungiyar har ila yau ta nemi kotun da ta hana gwamnatin tarayyar aiwatar da wani mataki da ta ce za ta dauka, na hukunta manema labarai ko kafafen yada labarai da suka yi amfani da shafin na Twitter.

Makonni biyu da suka gabata hukumomin Najeriya suka haramta amfani da shafin wanda suka ce yana barazana ga zaman lafiyar kasar.

Haramcin na zuwa ne bayan da kamfanin na Twitter ya goge wani sakon da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya wallafa wanda ya yi gargadi ga masu ta da kayar baya a kudu maso gabashin Najeriya, sakon da Twitter ya ce ya saba ka’idojinsa.

Sai dai a wannan kara da SERAP ta shigar a karshen makon nan, mai lamba FHC/ABJ/496/2021 a kotun ta Abuja, ta nemi da “a hana gwamnatin Shugaba Buhari, da hukumar kula da kafafen yada labarai ta NBC, Lai Muhammed da duk da wani da ke da hannu a lamarin,” yin katsalandan kan duk al’amuran da suka shafi kafafen sada zumunta da na yada labarai.

Wannan kara da SERAP ta shigar na zuwa ne kusan mako biyu, bayan da ta shigar da makamanciyarta a gaban kotun kungiyar kasashen ECOWAS.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...