Sarkin Bichi ya sauke Hakiman Kano saboda kin yi masa mubayi’a

Sarkin ya cire Hakimansa biyar cikin tare wadanda suke a Masarautar kan kin yi masa biyayya.
Image caption

Sarkin ya cire Hakimansa biyar cikin tare wadanda suke a Masarautar kan kin yi masa biyayya.

Mai martaba Sarkin Bichi Alhaji Aminu Ado Bayero ya sauke wasu hakimai saboda kin yi masa mubayi’a.

Hakimi biyar ne sarkin ya sauke inda tuni ya maye gurbinsu da wasu mutane.

Hakiman da aka cire sun hada da:

  • Madakin Kano Hakimin Dawakin Tofa Alhaji Yusuf Nabahani, wanda shi ne shugaban masu zaben Sarkin Kano.
  • Matawallen Kano Hakimin Minjibir Aliyu Ibrahim Ahmed.
  • Barden Kano Hakimin Bichi Alhaji Idris Bayero.
  • Hakimin Tsanyawa Alhaji Sarki Aminu.
  • Sarkin Bai Hakimin Dambatta Alhaji Mukhtar Adnan, daya daga masu zaben Sarkin Kano.

Sarkin Bai ya zama Hakimin tun 1954, abin da ya sa ya fi kowane Hakimi dadewa a masarsutar Kano, domin kuwa ya shafe shekara 64 yana Hakimci kafin a sauke shi a ranar Asabar din nan.

Shi kuma Barden Kano Hakimin Bichi Alhaji Idris Bayero, uba yake ga Sarkin Bichi Alhaji Aminu Ado Bayero.

Biyu daga cikin Hakiman da aka cire wato Madaki da Sarkin Bai na cikin mutum hudu da suka shigar da karar gwamnan Kano kan sababbin sarakunan da aka nada gaban kotu.

Suna kalubalantar kirkirar sababbin masarautu sannan suka nemi kotu ta hana wadanda aka yi kara sauke su daga mukamansu ko daukar wani mataki da zai taba aikinsu na masu zaben Sarki.

Wannan na zuwa ne bayan da majalisar jihar Kano ta sake yin wata doka wadda ta kafa sabbin masarautu guda hudu wadanda kotu ta soke a watan da ya gabata.

Kotun ta sanya ranar Talata domin fara sauraron karar.

Hakkin mallakar hoto
SALISHU TANKO YAKASAI/FACEBOOK

Image caption

Gwamna Ganduje ne ya kafa sabbin masarautun guda hudu inda ya ce za su kawo ci gaba a jihar, inda wasu kuma ke sukar shi da zargin ruguza tarihin Kano.

Kwanaki kadan bayan kafa dokar gwamnan Kano Abdullahi Ganduje, ya nada Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, a matsayin shugaban majalisar sarakunan jihar inda ya umurce shi da ya kira taron zauren.

Har yanzu dai Sarkin bai kira taron ba inda masarautar Kano ta sake maka gwamnatin jihar Kotu kan kafa sabbin masarautu a jihar.

Masarautar Kano na daga cikin wadanda suke da tarihi da shekaru da dama a kasar Hausa.

An yi sarakunan Habe sama da 40 kafin Fulani suka karbi mulki a shekarar 1806 inda Sarki mai ci a yanzu Muhammadu Sanusi II, wanda shi ne na 14 a jerin Fulani ke mulki bayan da ya gaji Ado Bayero, a 2014 wanda kuma shi ne mahaifin Sarki Bichi na yanzu, Aminu Ado Bayero.

More News

Kotu ta bayar da belin Hadi Sirika da Ć´arsa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da belin tsohon ministan harkokin sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da kuma wasu mutane uku kan...

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban RiĆ™on Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...