Mutane Takwas Sun Rasa Rayukansu a Wani Mummunan Hadarin Mota

Akalla mutane takwas sun mutu a wani mummunan haɗarin mota da ya faru da safiyar Alhamis a kan babban titin Legas zuwa Ibadan, kusa da gadar Kara Bridge, wajen da ake kira Berger, a wajen Legas.

Shaidun gani da ido sun ce haɗarin ya haɗa da manyan motoci masu ɗaukar kaya da dama. Wata daga cikin motocin ta faɗa cikin rafin Kara, yayin da wasu biyu suka haɗu suka kama da wuta, abin da ya haifar da firgici da cunkoson ababen hawa a wannan babbar hanya da aka sani da cinkoso.

Jami’an ‘Yan Sanda na Najeriya tare da Hukumar Kula da Harkokin Zirga-zirga ta Jihar Legas (LASTMA) sun isa wurin da gaggawa domin dawo da tsari da kuma jagorantar aikin ceto da kashe wuta.

A cikin sanarwar da LASTMA ta wallafa ta hanyar shafinta na X (Twitter), hukumar ta tabbatar da cewa mutane takwas ne suka mutu a haɗarin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]