Mutane Takwas Sun Rasa Rayukansu a Wani Mummunan Hadarin Mota

Akalla mutane takwas sun mutu a wani mummunan haɗarin mota da ya faru da safiyar Alhamis a kan babban titin Legas zuwa Ibadan, kusa da gadar Kara Bridge, wajen da ake kira Berger, a wajen Legas.

Shaidun gani da ido sun ce haɗarin ya haɗa da manyan motoci masu ɗaukar kaya da dama. Wata daga cikin motocin ta faɗa cikin rafin Kara, yayin da wasu biyu suka haɗu suka kama da wuta, abin da ya haifar da firgici da cunkoson ababen hawa a wannan babbar hanya da aka sani da cinkoso.

Jami’an ‘Yan Sanda na Najeriya tare da Hukumar Kula da Harkokin Zirga-zirga ta Jihar Legas (LASTMA) sun isa wurin da gaggawa domin dawo da tsari da kuma jagorantar aikin ceto da kashe wuta.

A cikin sanarwar da LASTMA ta wallafa ta hanyar shafinta na X (Twitter), hukumar ta tabbatar da cewa mutane takwas ne suka mutu a haɗarin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]