Mutane Sama da 100 Sun Mutu a Rikicin Ƙasashen Afghanistan da Pakistan

Aƙalla mutum 100 ne suka rasa rayukansu sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin ƙasashen Afghanistan da Pakistan.

Majiyoyi daga sashen binciken gawarwaki na ma’aikatar lafiyar Afghanistan sun shaida wa BBC cewa an karɓi gawarwaki sama da 100 bayan hare-haren da aka kai a ranar Litinin.

Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin gawarwakin sun lalace matuƙa har ba a iya gane su ba saboda tsananin raunukan da suka samu.

Gwamnatin Afghanistan tare da sashen agajin gaggawa na Majalisar Ɗinkin Duniya sun bayyana cewa an kai hari kan wani asibiti da ke kula da masu fama da matsalolin ƙwaƙwalwa.

Sai dai a nata ɓangaren, Pakistan ta ce hare-haren sun nufi abin da ta kira “ma’ajiyar makaman ƴanbindiga,” tana mai kare matakin da ta ɗauka.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]