Mutum 32 Sun Mutu Bayan Motar Bas Ta Faɗa Kwari A Pakistan



Aƙalla mutum 32 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 16 suka samu raunuka sakamakon hatsarin wata motar bas da ta faɗa cikin wani kwari a yankin kudu maso yammacin Pakistan.

Rahotanni sun bayyana cewa motar na kan hanyarta daga Quetta zuwa Peshawar ne lokacin da hatsarin ya faru a yankin tsaunukan Dana Sar da ke kan iyakar jihohin Balochistan da Khyber Pakhtunkhwa.

Wani jami’i a asibitin Zhob ya shaida wa BBC cewa motar na ɗauke da mutum 48 ciki har da mata da yara ƙanana lokacin da lamarin ya auku.

Binciken farko ya nuna cewa motar ta ƙwace wa direba ne yayin da yake ƙoƙarin saukowa daga kan tsaunin kafin ta faɗa cikin kwarin.

Jami’ai sun ce an kai waɗanda suka ji rauni zuwa asibitin hedikwatar gundumar Zhob, yayin da aka kai gawarwakin mamatan domin tantancewa kafin mayar da su zuwa garuruwansu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]