Mutum 32 Sun Mutu Bayan Motar Bas Ta Faɗa Kwari A Pakistan



Aƙalla mutum 32 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 16 suka samu raunuka sakamakon hatsarin wata motar bas da ta faɗa cikin wani kwari a yankin kudu maso yammacin Pakistan.

Rahotanni sun bayyana cewa motar na kan hanyarta daga Quetta zuwa Peshawar ne lokacin da hatsarin ya faru a yankin tsaunukan Dana Sar da ke kan iyakar jihohin Balochistan da Khyber Pakhtunkhwa.

Wani jami’i a asibitin Zhob ya shaida wa BBC cewa motar na ɗauke da mutum 48 ciki har da mata da yara ƙanana lokacin da lamarin ya auku.

Binciken farko ya nuna cewa motar ta ƙwace wa direba ne yayin da yake ƙoƙarin saukowa daga kan tsaunin kafin ta faɗa cikin kwarin.

Jami’ai sun ce an kai waɗanda suka ji rauni zuwa asibitin hedikwatar gundumar Zhob, yayin da aka kai gawarwakin mamatan domin tantancewa kafin mayar da su zuwa garuruwansu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]