Mutum Biyar Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Neja



Akalla mutum biyar sun rasa rayukansu, yayin da wasu takwas suka jikkata sakamakon wani hatsarin mota da ya faru a yankin Agaie da ke jihar Neja.

Jami’in Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), Hussaini Guregi, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya ce hatsarin ya rutsa da wata babbar mota mai ɗauke da fasinjoji da kuma tankar mai.

Rahotanni sun ce motar na kan hanyarta daga Gusau a jihar Zamfara zuwa Shagamu a jihar Ogun lokacin da hatsarin ya afku.

An bayyana cewa mutum biyar sun mutu nan take, yayin da aka kai waɗanda suka jikkata Asibitin Kwamishinan Agaie domin samun kulawar lafiya.

More from this stream

Recomended