Mutane biyu sun É“ace a yayin da aka ceto mutum uku a wani hatsarin jirgin ruwa a Adamawa

Mutane biyu ne suka ɓace a yayin da aka samu nasarar ceto wasu mutane uku a wani hatsarin jirgin ruwa a ƙaramar hukumar Gamadio dake jihar Adamawa.

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ita tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata.

Ladan Ayuba shugaban sashen ayyukan yau da kullum na hukumar NEMA a Yola shi ne ya jagoranci tawagar kai É—aukin gaggawa tare da mataimakin gwamnan jihar, Kaletapwa Farauta ya zuwa wurin da abun ya faru.

Shugaban karamar hukumar, Christopher Sofore ya yi wa mataimakin gwamnan bayanin abun da ya faru inda ya ce ana cigaba da aikin bincike domin gano gawarwakin mutane biyu.

Mataimakin gwamnan ya sanar da kafa wani kwamitin bincike da ya Æ™unshi jami’an tsaro na DSS, Æ´an sanda, jami’an kashe gobara, NEMA da kuma na hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Adamawa domin cigaba da gudanar da aikin gano mutanen biyu.

Ya kuma shawarci hukumomin da abin ya shafa da su samar da rigar kariya tare da tabbatar da cewa ana amfani da su domin kare faruwar irin haka nan gaba.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...