’Yan Sanda Sun Ceto Mutumin Da Aka Sace A Adamawa



Rundunar ’yan sandan jihar Adamawa ta ceto wani mutum da aka sace tare da kashe mutum biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a wani samame da ta kai.

Mutumin da aka ceto mai suna Alhaji Sidiki Isah ne, mai shekara hamsin da huɗu daga ƙauyen Tambo da ke ƙaramar hukumar Girei. Rahotanni sun ce masu garkuwar sun nemi kuɗin fansa na naira miliyan casa’in daga iyalansa.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun gano maboyar masu garkuwar ne bayan samun bayanan sirri. Ya ce an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar kungiyar CJTF.

A cewarsa, masu garkuwar sun buɗe wa jami’an tsaro wuta bayan sun hango su, amma jami’an sun mayar da martani tare da kashe mutum biyu daga cikin waɗanda ake zargi. Sauran sun tsere da raunukan harbi.

Nguroje ya ƙara da cewa an ceto wanda aka sace cikin koshin lafiya, sannan an ƙwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu, harsasai da wasu kayayyaki.

More from this stream

Recomended