Muna jan hankalin gwamnatin Kaduna kan rushe mana coci – CAN | BBC Hausa

Elrufai

Kungiyar mabiya addinin kirista reshen jihar Kaduna ta bayyana rashin jin dadinta dangane da yunkurin gwamnati na rusa cocin Anglican na Saint Geoges da ke Sabon garin Zaria, wadda aka gina a 1908.

An dai ce gwamnati na son rusa cocin ne da manufar fadada wata kasuwa da ke kusa da ita.

Shugaban kungiyar, Reverend John Hayab ya bayyana wa BBC cewa an sha yunkurin rusa majami`ar da nufin fadada kasuwar da ke makwabtaka da cocin ana fasawa saboda tarihinta.

“Yawancin wadanda suke shugabanci a yanzu ba a haife su ba lokacin da aka gina cocin”.

Reverend Hayab ya karyata cewa an bai wa cocin diyya “Muna zaune kawai sai muka ga wasika wai za a rushe coci saboda an biya kudin diyya. Ba bu wanda ya biya diyya”

“Na biyu wasikar kuma ba ta da kwanan wata a jikinta. Shi ya sa muke neman gwamnatin jihar ta Kaduna ta fada mana tana da masaniya kan wannan wasika idan ba haka ba kuma muna son ta hukunta duk mai hannu a al’amarin.”

  • Gobara ta tashi a Majami’ar Notre-Dame a Faransa
  • Da gaske ne gwamnatin Rivers ta rushe masallaci?

BBC dai ta yi kokarin tuntubar Kwamishinan harkokin cikin gida na jihar Kaduna, wanda shi ne mai magana da yawun gwamna, Mr Aruwan domin jin nasu bangaren, amma ba a yi nasara ba.

A Najeriya dai al`amuran da suka shafi addini ko ibada , kamar yadda masu lura da la`amura kan ce suna bukatar a yi kaffa-kaffa da su, sakamakon yadda suka haddasa kace-na-ce.

Ko da a `yan kwanakin baya ma, an yi ta kartar-kasa da murza gashin-baki tsakanin al`umar musulmi da gwamnatin jihar Rivers, bayan gwamnati ta share wani wuri da musulmin ke sallar juma`a.

Sai dai har zuwa yanzu dai gaskiyar maganar ta kasa fita. Yayin da musulmi ke cewa masallaci mallakinsu aka rusa, bangaren gwamnati kuma na cewa fili ne na Allah, kuma ba mallakin musulmin ba ne.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...