Jami’an ICPC sun yi bincike a gidan El-Rufai dake Abuja

Jami’an hukumar ICPC dake hana ci da karɓar rashawa sun gudanar da bincike a gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai  dake Abuja.

Muyiwa Adekeye mai taimakawa El-Rufai kan harkokin yaɗa labarai ya ce jami’an sun gudanar da bincike a gidan ranar Alhamis.

Adekeye ya bayyana haka ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafin sa na X .

Sakon ya bayyana cewa lauyan El-Rufai Ubong Akpan ya yi allawadai da binciken da bayyana da haramtacce kuma wanda ya sabawa matakan shari’a da kuma hakkin dan adam.

Okoh Odey mai magana da yawun hukumar ta ICPC bai ce komai ba akan binciken da hukumar ta gudanar.

A ranar Laraba ne hukumar ta ICPC ta sanar da cewa tana tsare da tsohon gwamnan sakamakon binciken da take gudanarwa.

El-Rufai ya faɗa hannun jami’an hukumar ta ICPC ne daga hannun hukumar DSS bayan da ya shafe kwanaki biyu a hannun hukumar EFCC yana amsa tambayoyi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]