Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) a jihohin Arewa 19 da Abuja tare da kungiyar limaman kirista ta Ecumenical Synods of Bishops, Archbishops, Apostles and Senior Clergy sun yi watsi da kalaman shugaban Amurka Donald Trump cewa Amurka ta dakatar da kashe-kashen Kiristoci a Najeriya.
Kungiyoyin sun ce ikirarin ba ya da tushe kuma ya saba da abin da ke faruwa a kasar, inda suka bayyana cewa matsalar rashin tsaro na ci gaba da addabar al’umma a sassa daban-daban na Najeriya.
Trump ya yi wannan ikirari ne yayin wani taro a Washington ranar Juma’a, inda ya ce matakin da sojojin Amurka suka dauka a Najeriya ya taimaka wajen dakile hare-haren da ake kai wa Kiristoci.
“Kamar yadda kuka sani, kwanan nan mun kai hari a Najeriya kuma mun dakatar da kisan kiyashin Kirista,” in ji Trump.
Ya kuma ce hare-haren sun yi tasiri kan masu kai hare-haren, yana mai cewa an kashe wasu shugabanninsu da mataimakansu.
CAN Ta Karyata Ikirarin Trump Kan Rage Kisan Kiristoci a Najeriya

