Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Mohammed Abubakar, ya lashe zaɓen fidda gwani na takarar gwamna a jam’iyyar APC, bayan ya doke manyan ‘yan takara ciki har da tsohon ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, da Bala Maijama’a A. Wunti, tsohon jami’in kamfanin mai na ƙasa NNPLC.
Rahotanni sun nuna cewa an samu jinkiri wajen sanar da sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Alhamis, inda aka bayyana sakamakon a safiyar Asabar.
Mohammed Abubakar, wanda aka fi sani da MA, ya taɓa fuskantar ƙalubale a siyasa a baya, inda ya sha kaye a hannun Bala Mohammed na jam’iyyar PDP a zaɓen gwamnan jihar a shekarar 2019.
A gefe guda kuma, Yusuf Tuggar na daga cikin ministocin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da suka ajiye muƙamansu domin tsayawa takara a zaɓen 2027, bayan ya yi murabus daga muƙaminsa a ƙarshen watan Maris domin shiga fagen siyasa.
Mohammed Abubakar Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Bauchi A APC

