Al’amuran tsaro sun fara samun sauyi sakamakon yadda jama’ar gari suka fara mayar da martani, ta hanyar cafke da kuma yin garkuwa da iyalan ‘yan bindiga.
Har wasu matasan yankin Birnin Magaji na jihar Zamfara sun yi garkuwa da wasu matan aure na ‘yan bindiga, ciki har da wata mai juna biyu.
Matasan sun yi ikirarin cewa sun dauki wannan mataki ne bayan da ‘yan bindigan suka sace mutanen yankin su bakwai da ababen hawansu.
Matasan sun ce ba za su saki matan ‘yan bindigan da suka damke, suke garkuwa da su ba, har sai mazansu sun sako wasu mutanen yankin da suka sace a baya baya nan.