Matasan gari a Zamfara sun yi garkuwa da iyalan ‘yan bindiga

Al’amuran tsaro sun fara samun sauyi sakamakon yadda jama’ar gari suka fara mayar da martani, ta hanyar cafke da kuma yin garkuwa da iyalan ‘yan bindiga.

Har wasu matasan yankin Birnin Magaji na jihar Zamfara sun yi garkuwa da wasu matan aure na ‘yan bindiga, ciki har da wata mai juna biyu.

Matasan sun yi ikirarin cewa sun dauki wannan mataki ne bayan da ‘yan bindigan suka sace mutanen yankin su bakwai da ababen hawansu.

Matasan sun ce ba za su saki matan ‘yan bindigan da suka damke, suke garkuwa da su ba, har sai mazansu sun sako wasu mutanen yankin da suka sace a baya baya nan.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]