Masarautar Kano: Ba mu ce a tsige Sarki Sanusi ba – KCSF | BBC Hausa

Sarki Sanusi da Ganduje

Hakkin mallakar hoto
Kano Government

Gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Kano ta nisanta kan ta daga wata wasika da ke cewa kungiyar ta yi kira ga gwamnan Kano ya tsige Sarki Muhammadsu Sanusi II daga kujerarsa.

Tun farko dai sakataren yada labaran gwamnatin jihar ne Abba Anwar ya fitar da sanarwa cewa kungiyar ta rubuta masu wasika tana neman Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da ya yi hakan.

A wata sanarwa da ta fitar a yau Juma’a, Kano Civil Society Forum ta ce “kage aka yi mana domin bata mata mana suna”.

Ta kara da cewa: “Abin takaici ne yadda wasu mutane da ba su bayyana kan su ba suka yi amfani da sunan kungiyar suka nemi gwamnan ya cire sarki daga mukaminsa.

“Bisa wannan dalili ne muke amfani da wannan damar domin nisanta kammu daga wannan batu na wasu kungiyoyi marasa kan-gado.”

Wannan na zuwa ne rana guda da wata sanarwar ta fito daga masarautar Kano, wadda ke cewa Sarki Sanusi ya karbi mukamin Shugabancin Majalisar Sarakunan Kano da Ganduje ya nada shi.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...