Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam’iyar NNPP ta karÉ“i magoya bayan jam’iyar APC da dama a jihar Kano.

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karÉ“i masu sauya sheÆ™ar ya zuwa jam’iyar ta APC da suka fito daga Æ™ananan hukumomin Bagwai da Shanono a madadin gwamnan jihar a gidan gwamnatin jihar Kano.

Wata sanarwa da ofishin mataimakin gwamnan ya fitar ta bakin, Ibrahim Garba Shu’aibu ta ce Gwarzo ya jaddada buÆ™atar fifita haÉ—in kai a jam’iyar inda ya tabbatar da za a kula da kowa ba tare da nuna bambanci ba.

Gwarzo ya ce gwamnatinsu ta mayar da hankali wajen aiwatar da tsare-tsare da za su amfani al’umma inda ya yi kira ga mutanen jihar su cigaba da basu goyon baya.

Da yake jawabi tun da farko jagoran masu sauya sheƙar, Alhaji Haruna Babangida Abbas (Kosasshe) ya ce ingancin shugabancin gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma salon gwamnatinsa na daga cikin dalilinsu na sauya sheƙar ta su.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...