Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin a É—aura musu aure.

Gwamnan ya rattaba hannu ne akan dokar a wani ƙwarya-ƙwaryar biki da aka gudanar a gidan gwamnati jihar da ya samu halartar shugaban majalisar dokokin jihar.

A cewar mai magana da yawun gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa daga yanzu babu wani aure da za a É—aura a jihar ba tare da an gabatar da takardar shedar yin gwaje-gwajen ba

Gwaje-gwajen sun haÉ—a da na ciwon hanta, cutar HIV, Æ™wayoyin halitta da kuma sauran cututtukan da za iya É—auka ta hanyar jima’i.

Ya ce dokar ta zama dole domin kawo ƙarshen yaran da ake haifa da cutar sikila, HIV da kuma cutar hanta.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...