Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Naɗa Masu Bada Shawara 20

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya naɗa masu bashi shawara su 20.

Shugaban majalisar, Ahmad Lawan shi ne ya gabatar bukatar shugaban ƙasar dake cikin wata wasikar da ya aikewa majalisar.

Bayan karanta wasikar, Sanata Ibrahim Gobir mai wakiltar mazabar Gabashin Sokoto ya bukaci majalisar da ta amince da bukatar shugaban ƙasar.

Kudirin na Gobir ya samu goyon bayan shugaban marasa rinjaye na majalisar Sanata Philip Aduda.

Majalisar Dattawan ta bawa kudirin kulawar gaggawa inda ta amince da bukatar nan take.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]