Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Naɗa Masu Bada Shawara 20

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya naɗa masu bashi shawara su 20.

Shugaban majalisar, Ahmad Lawan shi ne ya gabatar bukatar shugaban ƙasar dake cikin wata wasikar da ya aikewa majalisar.

Bayan karanta wasikar, Sanata Ibrahim Gobir mai wakiltar mazabar Gabashin Sokoto ya bukaci majalisar da ta amince da bukatar shugaban ƙasar.

Kudirin na Gobir ya samu goyon bayan shugaban marasa rinjaye na majalisar Sanata Philip Aduda.

Majalisar Dattawan ta bawa kudirin kulawar gaggawa inda ta amince da bukatar nan take.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar ƙera bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...